Mun kama mutanen da mu ke zargi da kashe DPO Rano – Kiyawa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da cewa ta kama mutanen da ake zargi da kisan gillar da aka yiwa Babban baturen yan sanda na karamar hukumar Rabo.

Ya bayyana alhini da jimami bisa mummunan kisan gillan da aka yi wa Baturen ‘Yan Sanda na Rano (DPO), CSP Baba Ali, yayin da yake bakin aiki.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar Yansandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Rundunar Yan Sandan ta kalli Wannan kisa na rashin hankali da al’umma suka masa mummunar suka a matsayin mummunan hari ga zaman lafiyar al’umma da kuma cin mutunci ga jajircewar jami’an ‘yan sanda da ke fuskantar haɗari kowace rana don kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Mun Gamsu da Samar da Kungiyar Kwarya ta bi Kwarya -Mai Rago

Sai dai Rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa an gurfanar da duk masu hannu a wannan ta’asa a gaban kotu. Bayan gudanar da bincike, an kama mutane 41, ciki har da wadanda aka same su dumu-dumu da hannu a cikin lamarin.

‘Yan sanda na ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da cewa ba a bar kowa ba cikin wadanda suka aikata wannan aika-aika.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, PhD, sfipma, mnim, mnips, masis, ya tabbatar wa al’umma cewa rundunar zata cigaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin Jihar bakidaya. Ya sake nanata cewa ba za a bar kowanne mai hannu a wannan ta’asa ba har sai an gurfanar da shi a gaban shari’a.

InShot 20250309 102403344

Rundunar na godiya ga fahimta, ta’aziyya da hadin kai da jama’a ke basu, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da zama cikin natsuwa da bayar da cikakken goyon baya ga ‘Yan Sanda a wannan bincike. Za mu ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen kare al’umma, tare da tabbatar da cewa duk wanda ya nemi dagula zaman lafiya, za a hukunta shi yadda ya kamata.

Hakazalika, rundunar ta karrama marigayi CSP Baba Ali, tare da yabawa jarumta da sadaukarwar jami’anmu da ke ci gaba da fuskantar haɗura don kare jihar mu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...