Gwamnatin Kano ta kama na’urorin da ake buga hotunan batsa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

A wani salo na tabbatar da doka tare da kawo tsafta a bangaren Dab’i, Hukumar tace fina-finai da Dab’i ta Jahar Kano karkashin jagorancin Alh. Abba El-mustapha ta kara yin nasarar ganowa tare da kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a cikin wasu unguwannin Jahar Kano wanda suka hada da komfuyutoci da Kuma injinan buga hotuna wato (Printers).

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ya aikowa Kadaura24.

Da yake holan kayan da Hukumar ta kama Alh. Abubakar Zakari Garun Babba darakan Dab’i na hukumar ya bayyana guraren da aka kama wannan kaya sun hada da wasu unguwani a karamar Hukumar birnin da Kuma wasu kauyuka na karamar Hukumar Wudil.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Garun Babba ya nuna taikacinsa kan yadda wasu ke fakewa da Sana’ar buga takardun watau photocopy inda suke buga hotunan batsa, inda ya kara da cewa ko kusa ko alama Hukumar bazata lamunci hakan ya cigaba da faruwa a fadin Jahar Kano ba.

Kawo ya wannan lokaci Hukumar na cigaba da rike kayan inda take dakon shawarar lauyoyinta domin daukar mataki na gaba.

InShot 20250309 102403344

A karshe Garun Babba ya gargadi masu sana’ar buga takardu dasu shiga taytayinsu domin gujewa fushin doka. Ya kuma kara yin kira ga al’ummar Jahar Kano tare da jami’an tsaro da su cigaba da bawa Hukumar cikakken goyan baya da hadin Kai ta yadda za’a kawo karshen irin wannan aiyukan a fadin Jahar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...