Mun Gamsu da Samar da Kungiyar Kwarya ta bi Kwarya – Mai Rago

Date:

Daga Zaharadden Sale

 

Samar da kungiyoyin mata, abune da zai karfafa ci gaban al’umma la’akari da irin gudummarwar da suke bayarwa tun daga tushe,

Shugaban karamar hukumar Dawakin Kudu Alhaji Sani Ahmad Mairago ne ya bayyana haka a yayin kaddamar da sabuwar kungiyar kwarya tabi kwarya da akayi a garin Tamburawa, a karamar hukumar Dawakin Kudu.

Mairago Wanda kansilan mazabar Tamburawa Alhaji Garba Auwal ya wakilta, ya Yabawa shugabannin kungiyar bisa tunani da hangen nesa na Samar da kungiyar a wannan lokaci, inda yace karamar hukumar zata hada hannu da kungiyar wajen ayyukan cigaba a yankin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

A jawabinta Shugabar kungiyar Hajiya Salma Alhaji Gambo ta bayyana manufofin kungiyar da suka hadar da hada kan mata Dan taimakawa juna a fanin ilimi , kiwon lafiya da tallafawa cigaban kananan yara a garin Tamburawa da kewaye

Yadda Mijina ya sake ni bayan ya damfare ni – Mansura Isa

A nasa jawabin tsohon Dan majalisar tarayya na karamar hukumar Dawakin Kudu Mustafa Bala Dawaki Maigidan Ruwa Wanda tsohon Dan majalisa Jiha Muazzam El Yakub ya wakilta, ya Yabawa kungiyar bisa managartan tsatsare da bijiro dasu tare da yin alkawarin aiki kafada da kafada da kungiyar Dan Samar da Kyakkyawan Yanayi a fanin ilimin da sana’a.

InShot 20250309 102403344

Da yake jawabi Uban kungiyar Kuma dagacin garin Tamburawa Alhaji Auwalu Dantube yabawa shugabannin kungiyar yayi bisa jajircewar su na ganin kungiyar ta kafu abin dayace Hakan wata alamace ta samun nasara, daganan sai ya godewa daukacin bakin da suka halarci taron Kuma suka bada gudummmawar kudade da littattafai dan karfafawa kungiyar,

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...