Daga Ummahani Abdullahi Adakawa
Mai Martaba Sarkin Kano na 16 Malam Muhammad Sanusi II ne ya bukaci gwamnatin tarayya da ta dawo da nada Amirul Hajji na kasa saboda muhimmancin da hakan ke da shi.
Kadaura24 ta rawaito Sarki Sanusi II ya bayyana hakan yayin da ya karbi tawagar Shugabannin hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Kano a a fadarsa.

Sarkin ya jaddada muhimmancin dawo da nadin Amirul Hajj na kasa, wanda zai rika jagoran tawagar alhazan Najeriya a yayin gudanar da aikin hajji a chan kasa mai tsarki .
Ya kara da cewa nadin Amirul Hajj ya samo asali ne tun a zamanin Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam), wanda ya karfafa nadin shugabannin da za su jagoranci al’umma a irin wadannan tafiye-tafiye na ibada.
Hajjin Bana: An sanya ranar da Alhazan Kano za su fara tashi zuwa Saudiyya
Ya kuma jaddada cewa nadin Amirul Hajj na kasa ya zama duba da irin rawar da ya ke tawa a yayin aikin Hajji .
A nasa bangaren, Darakta Janar na Hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya ce sun je fadar Sarkin ne domin gayyatar Sarkin domin ya halarci taron aikin Hajji na gwaji da za a gudanar a sansanin Hajji.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Sulaiman Abdullahi Dederi ya aikowa Kadaura24, ya ce Alhaji Lamin Rabi’u ya kara da cewa Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin fara jigilar Alhazai da aka shirya farawa a ranar 13 ga watan Mayun 2025.