Da dumi-dumi: NNPC zai raba man fetur kyauta

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kamfanin albarkatun mai na Nigeria NNPC ya sanar da fara bayar da man fetur kyauta ga masu ababen hawa a babban birnin tarayya Abuja da kuma jihar Bauchi.

A wata sanarwa da kamfanin ya aikowa Kadaura24, ya ce kamfanin zai raba man ne kyauta a wasu sabbin gidajen mai mallakin kamfanin da aka bude a Abuja da Jihar Bauchi.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Sanarwar ta ce ” NNPC ya sake bude sabbin gidajen man ne a kokarinsa na ganin ya saukakawa yan Nigeria sun sami man fetur cikin sauki kuma a kusa da su.

Gwamnatin Kano, za ta kula alakar Noma, kasuwanci da makamashi da kasar Morocco

” Za mu bayar da man ne ga masu motoci da babura, domin nuna godiya ga al’umma bisa irin hadin kan da suke ba mu a ko da yaushe”.

InShot 20250309 102403344

” A Abuja kan titin Airport Road za mu baiwa masu babura kimanin 200 lita 5 – 5 na man fetur kyauta, yayin da kuma a sabon gidan man NNPC dake Kano – Ningi Road mu ka riga muka bayar da kyautar man ga kwastomomi da suka fara zuwa sayan mai a wurin mu a ranar 17, ga watan Afirilun 2025″.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...