Kungiyar samarin Tijjaniyya ta yi Allah – wadai da hukuncin Kotun ECOWAS

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kungiyar Samarin Tijjaniya ta kasa tace bata goyon bayan Hukuncin da kotun ECOWAS ta yanke akan batanci ga Janibin Annabi muhammadu SAW.

A wata sanarwa da Kungiyar ta fitar Mai dauke dasa hannun Babban Sakatare Shehu Tasiu Ishaq da sakataren yada labarai Abubakar Balarabe Kofar Naisa Kungiyar tayi tir da Allah wadai da Hukuncin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kungiyar tace yin Hukuncin ya sabawa dokokin addinin musulunci, Wanda kuma duk wani Hukuncin da zaici Karo da dokokin Ubangiji bazasu goyi bayansa ba.

Majalisar dokokin Kano da Freedom Radio sun fara musayar kalamai

Daga nan kungiyar Samarin Tijjaniyya ta kasa tayi kira ga Gwamnati a kowane mataki da lallai a tabbatar dabin dokokin da suka tabbatar da tsarin addinin musulunci akan duk Wanda ya keta alfarmar fiyayyen halitta kamar yadda yake a kundin dokokin shari’ar Musulunci.

Kungiyar kuma ta yabawa Gwamnatin Jihar Kano bisa yadda ta jaddada matsayinta na tabbatar da dokokin da suka shafi hukunta duk Wanda yayi batanci ga Janibin Annabi muhammadu SAW Wanda daman tuni dokokin sun kasance na Gwamnatin Jihar ne.

InShot 20250309 102403344

A don hakane ma Kungiyar ta sake jaddada bukatar mabiya dariqar Tijjaniyya da sauran al’umar Musulmi su cigaba da kasancewa masu son zaman lafiya da kwanciyar hankali da kuma bin dokokin addinin musulunci.

Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta kasa ta sake bukatar Musulmi su dunga kasancewa masu yin ladabi da biyayya tareda kare duk wata Martaba ta Janibin Annabi muhammadu SAW a kalamansu na yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda gwamnan Kano ya ke rabon kujerun aikin hajjin bana kamar gyada

Daga Rahama Umar Kwaru Al'ummar jihar Kano na cigaba da...

An sulhunta tsakanin Nigeria da Nijar

Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta...

Neman shahara: Hukumar Hisbah ta kama Matashin da ya lashi al’aurar akuya

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Jami’an hukumar Hisbah ta jihar Kano...

2025 Ina Fatan Za ‘ a Yi Aikin Hajjin Da Ba a Taba Yin Irin Sa Ba a Nijeriya – Sheikh Abdullahi Sale Usman

By Ismail Yusuf Makwarari Shugaban hukumar kula da aikin Hajji...