Damina: Gwamnati ta bayyana jihohin da za su iya fuskantar ambaliyar ruwa a Nigeria

Date:

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za a fuskanci mamakon ruwan sama da zai haddasa ambaliyar ruwa a jihohi 30 da kuma Abuja babban birnin tarayyar kasar a daminar bana ta 2025.

Ministan albarkatun ruwa, Joseph Utsev, ne bayyana haka a ranar Alhamis a yayin gabatar da hasashen kan ambaliyar ruwa wanda hukumar da ke kula da rafuka ta kasar NIHSA ta yi.

FB IMG 1744283415267
Talla

Jihohin da za su iya fuskantar ambaliyar ruwan sun hadar da Legas da Ogun da Abia da Ondo da Adamawa da Akwa Ibom da Anambra da Bauchi da Benue da Borno da Bayelsa da Cross-River.

Sauran su ne Delta da Ebonyi da Edo da Gombe da Imo da Jigawa da Kebbi da Kogi da Kwara da Nasarawa da Neja da Osun da Oyo da Rivers da Sokoto da Taraba da Yobe da Zamfara da kuma birnin tarayya Abuja.

Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Ministan ya ce wasu bangarori na yankin kudu maso kudancin kasar za su fuskanci ambaliya ta gabar tafkuna da rafuka.

Jihohin sun hadar da Bayelsa da Cross-River da Delta da Rivers, yayin da Akwai-Ibom da kuma Edo za su kasance cikin mummunan hadarin ambaliyar ruwa.

InShot 20250309 102403344

A cewar ministan, ambaliyar ruwa ita ce babbar masifar yanayin da ke daidaita mutane da albarkatun kasa a Najeriya sannan kuma sauyin yanayi ne ke kara hadarin afkuwa ambaliyar.

Joseph Utsev, ya ce jihohin da suka hadar da Abia da Benue da Legas da Bayelsa da Rivers da kuma na daga cikin jihohin da ke cikin hadarin fuskantar ambaliyar ruwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar samarin Tijjaniyya ta yi Allah – wadai da hukuncin Kotun ECOWAS

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Kungiyar Samarin Tijjaniya ta kasa tace...

Majalisar dokokin Kano da Freedom Radio sun fara musayar kalamai

Majalisar dokokin jihar Kano ta nemi al'ummar jihar Kano...

2027: Shugabannin APC a Kano ta Kudu sun mika bukatarsu ga Sanata Kawu Sumaila

Shuwagabannin jam’iyyar APC da Sakatarorin su na mazabar Kano...

Tinubu ya sake ƙaddamar da aiki titin Abuja zuwa Kaduna

Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gina...