Musa Iliyasu Kwankwaso, Rabi’u Sulaiman Bichi sun kama aikin da Tinubu ya ba su

Date:

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa

 

Sabon Shugaban hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are Engr. Rabi’u Sulaiman Bichi da sauran abokan aikina su biyar sun shiga ofis domin kama aiki a matsayin Shugabannin hukumar.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito watanni kusan hudu da suka gabata Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya nada Rabi’u Sulaiman Bichi a matsayin shugaban hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are da kuma Musa Iliyasu Kwankwaso a matsayin babban daraktan kudi da harkokin mulki na hukumar da karin wasu mutane 3.

A ranar talata ne sabbin Shugabannin suka kama aiki bayan da Masoya da magoya bayansu suka yi musu rakiya domin shaida yadda za su kama aikin.

InShot 20250309 102403344

Da yake jawabin shugaban hukumar Engr. Rabi’u Sulaiman Bichi ya yiwa al’ummar Jihohin Kano Jigawa da Bauchi albishirin inganta harkokin noma da samar da aiyukan yi ga matasa masu tarin yawa.

” Wannan ma’aikatar babbar ma’aikata ce da za mu yi amfani da ita wajen tallafawa yan jam’iyyar APC, don haka nake sanar da cewa ba sai kun wahalar da kanku wajen zuwa Wannan hukuma ba za mu tsare-tsaren da tallafin mu zai iske ku duk inda kuke”. Inji Engr. Rabi’u Sulaiman

Gwamnatin Nigeria za ta ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira

Shi ma a nasa jawabin Babban Daraktan Kudi da Mulki na hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso ya yi alkawarin duk duk mai yiwuwa don inganta rayuwar al’ummar Jihohin Kano Jigawa da Bauchi.

” Muna godewa dukkanin masoya da magoya bayanmu da suka rako mu wannan ma’aikatar kuma muna baku tabbacin za ku dara sosai, don haka a cigaba da yi mana Addu’ar Allah ya ba mu ikon sauke nauyin da Shugaban kasa ya dora mana”. Inji Musa Iliyasu

Musa Iliyasu Kwankwaso ya kuma godewa shugaban kasa Bola Tinubu da Shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje bisa yadda suka ba su Wannan dama don hidimtawa al’ummar Jihohin Kano Jigawa da Bauchi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar samarin Tijjaniyya ta yi Allah – wadai da hukuncin Kotun ECOWAS

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Kungiyar Samarin Tijjaniya ta kasa tace...

Majalisar dokokin Kano da Freedom Radio sun fara musayar kalamai

Majalisar dokokin jihar Kano ta nemi al'ummar jihar Kano...

2027: Shugabannin APC a Kano ta Kudu sun mika bukatarsu ga Sanata Kawu Sumaila

Shuwagabannin jam’iyyar APC da Sakatarorin su na mazabar Kano...

Tinubu ya sake ƙaddamar da aiki titin Abuja zuwa Kaduna

Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gina...