Musa Iliyasu Kwankwaso, Rabi’u Sulaiman Bichi sun kama aikin da Tinubu ya ba su

Date:

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa

 

Sabon Shugaban hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are Engr. Rabi’u Sulaiman Bichi da sauran abokan aikina su biyar sun shiga ofis domin kama aiki a matsayin Shugabannin hukumar.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito watanni kusan hudu da suka gabata Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya nada Rabi’u Sulaiman Bichi a matsayin shugaban hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are da kuma Musa Iliyasu Kwankwaso a matsayin babban daraktan kudi da harkokin mulki na hukumar da karin wasu mutane 3.

A ranar talata ne sabbin Shugabannin suka kama aiki bayan da Masoya da magoya bayansu suka yi musu rakiya domin shaida yadda za su kama aikin.

InShot 20250309 102403344

Da yake jawabin shugaban hukumar Engr. Rabi’u Sulaiman Bichi ya yiwa al’ummar Jihohin Kano Jigawa da Bauchi albishirin inganta harkokin noma da samar da aiyukan yi ga matasa masu tarin yawa.

” Wannan ma’aikatar babbar ma’aikata ce da za mu yi amfani da ita wajen tallafawa yan jam’iyyar APC, don haka nake sanar da cewa ba sai kun wahalar da kanku wajen zuwa Wannan hukuma ba za mu tsare-tsaren da tallafin mu zai iske ku duk inda kuke”. Inji Engr. Rabi’u Sulaiman

Gwamnatin Nigeria za ta ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira

Shi ma a nasa jawabin Babban Daraktan Kudi da Mulki na hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso ya yi alkawarin duk duk mai yiwuwa don inganta rayuwar al’ummar Jihohin Kano Jigawa da Bauchi.

” Muna godewa dukkanin masoya da magoya bayanmu da suka rako mu wannan ma’aikatar kuma muna baku tabbacin za ku dara sosai, don haka a cigaba da yi mana Addu’ar Allah ya ba mu ikon sauke nauyin da Shugaban kasa ya dora mana”. Inji Musa Iliyasu

Musa Iliyasu Kwankwaso ya kuma godewa shugaban kasa Bola Tinubu da Shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje bisa yadda suka ba su Wannan dama don hidimtawa al’ummar Jihohin Kano Jigawa da Bauchi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...