Hawan Sallah: Ƴansanda sun sake gayyatar Hadimin Sarki Sanusi kan zargin bijirewa umarni

Date:

 

Rundunar ƴansandan jihar Kano ta gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku domin amsa tambayoyi kan zargin saɓa wa umarnin da ƴansandan su ka bayar na haramta Hawan Sallah a Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa  da mai magana da yawun rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanyawa hannu kuma aka aikowa Kadaura24.

Ya ce rundunar ta jaddada matsayinta na haramta Hawan Salla a faɗin jihar, kuma duk wanda aka samu da laifin saɓa umarnin zai ɗanɗana kuɗarsa.

InShot 20250309 102403344
Talla

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a ranar Juma’ar da ta gabata ne dai  rundunar ƴansandan jihar ta fitar da sanarwar haramta Hawan Sallah a Kano bayan da ta ce ta samu bayanan sirri na wasu ɓata-gari da ke da aniyar haifar da tashin hankali a lokacin hawan.

Hotunan yadda aka yi Jana’izar Galadiman Kano

Haka kuma sanarwar ta ce kwamishinan ƴansandan jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori ya kafa wani kwamitin ƴansanda mai mambobi takwas domin gudanar da bincike kan tashin hankalin da aka samu a ranar Sallah lokacin da tawagar Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi ke komawa gida bayan jagorantar Sallar Idi.

A lokacin da aka samu hatsaniyar dai an kashe wani jami’in sintiri tare da raunata wani da ke aikin bayar da tsaro ga tawagar sarkin na 16.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...