Hukumar Zakka ta Kano ta Fara Rabawa Mabukata Zakka

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

Akalla kimanin mabukata maza da mata 500 ne su ka amfana da zakkar Naira dubu Ashirin- ashirin Wanda hukumar zakkah da hubusi ta jihar Kano ta gudanar a yau Litinin da aka gudanar farfajiyar hukumar dake kan titin airport road.

Da yake jawabi ga ‘yan jarida shugaban hukumar zakkah da hubisi ta Jihar Kano Barista Habibu Dan almajiri Fagge ya ce wannan zakkah wasu manyan attajirai ne a jihar kano su ka fidda zakkar su su ka kuma mikawa hukumar zakkah da hubisi ta Jihar Kano don su rabawa mabukata.

InShot 20250309 102403344
Talla

Cikin wadanda suka Bayar da zakkar sun hadar da attajirin Dan kasuwar nan Alhaji Aminu Alhasan Dantata Wanda ya ba da( naira miliyan biyar)5000000 sai Kuma Alh.Mustapha Amasco Wanda shi ma ya ba da (naira miliyan biyar) 5000000 sai Kuma wani bawan Allah Wanda ya ba da dubu dari biyar, dukkaninsu domin a tallafawa mabuka, kamar yadda shugaban hukumar zakkah da hubisi ta Jihar Kano Barista Habibu Dan almajiri Fagge ya bayyana .

Sarki Aminu Ado Bayero ya fara daukar matakan gudanar da Hawan Sallah Karama a Kano

Shi ma a nasa Jawabin kwamashi na Daya a hukumar M.Nafi’u Umar Harazumi kira yayi ga mawada su cigaba da tallafawa hukumar wajen ba da zakkarsu ga hukumar domin rabawa ga mabukata .

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da zakkar sun yabawa hukumar sannan suka godewa wadanda suka ba da zakkar.

Wakilinmu ya bamu labarin cewa taron ya samu halartar al’umma dama .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hawan Sallah: Yansandan Kano sun gayyaci hadimin Sarki Sanusi II bayan mutuwar wani

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...

Barka da Sallah: Gwamnan Kano ya bukaci yan jihar su rungumi zaman lafiya da adalci

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Sarki Aminu da Sarki Sanusi sun bukaci gwamnati ta hukunta duk masu hannu a kisan Mafarautan Kano a Edo

Daga Aliyu Danbala Gwarzo da Sani Idris maiwaya   Mai Martaba...

Murtala Sule Garo ya yiwa Kanawa Barka da Sallah

Ina taya daukacin al’ummar Musulmi maza da mata musamman...