Ɗan Gwamnan Bauchi ya caccaki Dan Shugaban kasa Seyi Tinubu

Date:

Shamsuddeen Bala Mohammed, dan gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya yi kira ga Seyi dan shugaban kasa Bola Tinubu da kada ya maida matasan jihar almajirai idan ya zo jihar a ziyarce-ziyarce da ya ke yi zuwa jihohi.

PUNCH ta rawaito cewa, Mohammed, a wani sako da ya wallafa a Facebook a jiya Lahadi, ya bukaci Seyi da ya samarwa matasan Bauchi guraben ayyukan yi, da jari su fara kasuwanci, da horar da su kan kasuwanci na crypto, da sauran nau’o’in karfafawa maimakon raba musu abinci a roba.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ya ce, “ Lokacin da za a zo Bauchi, a ba wa matasan mu aikin yi, a basu Keke NAPEP, kuɗaɗe don fara kasuwanci, a karfafa su akan fasahar zamani, Wato ICT da horar da su kan kasuwancin crypto da sauransu.

“Don Allah, mu matasan Bauchi ba mu bukatar shinkafa da abinci a leda a cikin watan Ramadan. A koya wa matasanmu yadda ake kama kifi, maimakon ciyar da su na kwana guda.

“Ba almajirai ba ne.”

Iftila’i: An sanya dokar hana fita a Jigawa

Ya jaddada cewa matasan Bauchi ba sa bukatar tallafin abinci sai dai dama don dogaro da kai.

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa an hangi Seyi Tinubu yana raba abinci ga mabukata a ziyarar da ya kai wasu jihohin Arewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira

Matatar Dangote ta sanar da dakatar da sayar da...

Neman Kudi na zo Kannywood ba fadakarwa ba – Sadiq Sani Sadiq

    Fitaccen jarumi a Masana’antar Kannywood Sadik Sani Sadik ya...

Hatsari Guda Biyu da Su ka Canza Rayuwar Matashi Nuraddin, Amma ba su Dakushe Burinsa ba

Nuraddin ya fuskanci manyan jarabawa guda biyu a rayuwar...

Zargin Handama: Al’ummar Garin Danzaki Sun Nemi Agajin Gwamnan Kano

Daga Rabi'u Usman   Al'ummar garin Danzaki sun koka da yadda...