Shekarau ya magantu kan batun sake hadewarsu da Kwankwaso

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekaru ya ce yana da kyakkyawar alaƙa tsakaninsa da da jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

A hirarsa da BBC, Malam Shekarau ya nuna babu wata tattaunawa da nufin sulhu tsakaninsa da Rabiu Musa Kwankwaso, saɓanin rahotannin da ke cewa suna tattaunawa.

Ya ce babu wani sulhu tsakaninsa da jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

InShot 20250115 195118875
Talla

“Ni ban ma yarda a yi amfani da kalmar sulhu ba tsakanina da ɗan’uwana Rabiu Musa Kwankwaso ba.”

“Duk inda ka ji an ce sulhu, to rigima ake yi,” in ji Malam Shekarau.

Malam Ibrahim Shekaru ya ce babu wata matsalar dangantaka tsakaninsa da Kwankwaso.

Sabon Rikici ya Barke Tsakanin Jiga Jigan NNPP Kwankwasiyya a Kano

“Ba na rigama da shi, ba ya rigima da ni, muna gaisawa cikin mutunci da kuma ziyartar juna idan akwai sanadi,” in ji shi.

Tsoffin gwamnonin biyu na Kano Malam shekarau da Rabiu Musa Kwankwaso sun taɓa zama inuwa ɗaya a jam’iyyar APC da kuma NNPP ta Kwankwaso kafin Shekarau ya fice jam’iyyar.

Wasu rahotanni kuma na alaƙanta sasanci ne tsakanin ɓangarorin biyu domin buƙatun siyasa.

Sai dai Shekarau ya ce babu wata tattaunawa ta alaƙar siyasa tsakaninsa.

Ya ce suna tattaunawa tun yana APC da kuma bayan ya fice jam’iyyar Kwankwaso ta NNPP.

Fyade: Kotu ta yankewa wasu mutane 3 hukuncin kisa da yanke musu Mazakuta

“Muna magana da yan’uwantaka da juna tsakanina da Kwankwaso,” in ji Shekarau.

Ya ƙara da cewa babu wata rigima tsakaninsu da har za a yi zancen suna sasantawa tsakaninsu.

Batun sasanci tsakanin tsoffin gwamnonin na Kano biyu ya bijiro ne tun iƙirarin da Sanata AA Zaura ya yi cewa yana ƙoƙarin sasanta su, da kuma tsohon gwamnan Kano kuma shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa Abdullahi Umar Ganduje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...