Muhimmin Sakon Murtala Sule Garo ga Al’ummar Jihar Kano

Date:

 

Assalamu alaikum wa Rahmatullah

Ina mika sakon gaisuwa a yayin da al’ummar Musulmi a Najeriya da sauran sassan duniya daban-daban su ka fara gudanar da azumin watan Ramadan.

Tabbas wannan babbar dama ce a garemu ta inganta alakarmu da Allah maɗaukakin sarki ta hanyar habaka ibadarmu da neman yafiyarsa.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ina amfani da wannan dama wajen kira ga al’ummar musulmi dan yin koyi da dabi’un annabin rahama amincin Allah ya tabbata a gareshi wajen nuna tausayi da jinkai da karamci da kuma taimakawa marasa karfi.

Wannan wata mai alfarma dama ce ta tunawa da marasa karfi a cikinmu tun daga ‘yan uwa da makwafta har izuwa sauran al’umma.

Shekarau ya magantu kan batun sake hadewarsu da Kwankwaso

Hakazalika ina kira ga al’ummar jihar Kano da su dukufa wajen addu’o’in zaman lafiya da cigaba da yalwar arziki.

Ina yi wa kowa fatan alkairi. Allah ya karbi ibadinmu ya kuma sa mu kasance cikin bayin da zai yanta. Amin

Ramadan Kareem, Jumu’at Mubarak!

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...