Inganta tsaro: Kwamitin tsaro a Kano ta gana da masu ruwa da tsaki a harkar

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kwamin tsaro da yaki da fadan daba a jihar Kano ya gana da Daraktan hukumar DSS da Rundunar yan sanda da masu ruwa da sha’anin tsaro don inganta tsaro a Kano.

Shugaban kwamitin Dr. Yusuf K/Mata a ganawarsa da manema labarai ya ce sun kai ziyarar ne domin tattauna muhimman batutuwa da suka shafi tsaro tare da neman goyon bayan jami’an tsaro domin samun nasarar aikin da aka dorawa musu.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sannan ya bukaci hadin kan jami’an tsaron domin magance matsalar a Jihar Kano.

Da yake karin haske kwamishinan ma’aikatar yada kabarai da al’amuran cikin gida ta Jihar Kano, Comrd. Ibrahim Waiya, ya yabawa Rundunar Yan Sanda ta Jihar Kano, bisa rawar da suke takawa wajan inganta tsaro a Jihar.

Sabon Rikici ya Barke Tsakanin Jiga Jigan NNPP Kwankwasiyya a Kano

A jawabinsa AIG Salman Dogo Garba, ya yabawa gwamnan Jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf bisa samar da kwamitin.

Ya kuma ce a shirye suke su bada gudunmawa wajan magance matsalar tsaro a Jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

2027: Atiku Abubakar ya bayyana matsayarsa game da kasancewarsa a PDP

  Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin...

Cikakken Bayani Kan Yan Bindigar da Yansanda Su Ka Kama a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar yansanda ta kasa reshen jihar...

Gidauniyar Sheikh Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa magidanta 600 kayan abinchi a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Gidauniyar Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa...

Gwamna Abba Gida-gida Ya Kaddamar Da Gyaran Hanyoyi 17 A Babban Birnin Kano

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da...