Inganta tsaro: Kwamitin tsaro a Kano ta gana da masu ruwa da tsaki a harkar

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kwamin tsaro da yaki da fadan daba a jihar Kano ya gana da Daraktan hukumar DSS da Rundunar yan sanda da masu ruwa da sha’anin tsaro don inganta tsaro a Kano.

Shugaban kwamitin Dr. Yusuf K/Mata a ganawarsa da manema labarai ya ce sun kai ziyarar ne domin tattauna muhimman batutuwa da suka shafi tsaro tare da neman goyon bayan jami’an tsaro domin samun nasarar aikin da aka dorawa musu.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sannan ya bukaci hadin kan jami’an tsaron domin magance matsalar a Jihar Kano.

Da yake karin haske kwamishinan ma’aikatar yada kabarai da al’amuran cikin gida ta Jihar Kano, Comrd. Ibrahim Waiya, ya yabawa Rundunar Yan Sanda ta Jihar Kano, bisa rawar da suke takawa wajan inganta tsaro a Jihar.

Sabon Rikici ya Barke Tsakanin Jiga Jigan NNPP Kwankwasiyya a Kano

A jawabinsa AIG Salman Dogo Garba, ya yabawa gwamnan Jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf bisa samar da kwamitin.

Ya kuma ce a shirye suke su bada gudunmawa wajan magance matsalar tsaro a Jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...