Fyade: Kotu ta yankewa wasu mutane 3 hukuncin kisa da yanke musu Mazakuta

Date:

 

 

An yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya da kuma yanke mazakuta (Dandatsa) ga wasu mutum uku da aka bayyana sunayensu da John Moses, Yakubu Mohammed da Mustapha Musa, bayan kotu ta same su da laifin fyade a Kaduna.

LEADERSHIP ta rawaito cewa kwamishiniyar Ma’aikatar Kula da Harkokin Jin Kai da Ci gaban Al’umma ta Jihar Kaduna, Hajiya Rabi Salisu, ce ta bayyana hakan a Kaduna a jiya Laraba.

InShot 20250115 195118875
Talla

A cewar Kwamishiniyar, wacce ke da jajircewa wajen yaki da fyade da duk wani nau’in cin zarafin mata a jihar, ma’aikatar ta samu nasarar gurfanar da mutum uku da aka yanke musu hukunci kan laifin fyade daga watan Yuni 2024 zuwa watan Fabrairu 2025.

An sake samu tsaiko a shari’ar neman a hana kananan hukumomin Kano kudadensu

Ta bayyana hukuncin da aka yankewa mutanen a matsayin ci gaba mai kyau, kuma hakan zai zama izina ga wasu masu aikata irin wannan mugun aiki.

20250228 181700

“Ma’aikatar ta samu hukunci a ranar 7 ga watan Yuni 2024 a gaban Mai Shari’a Nana a shari’a mai lamba KDH/KAD/57c/2023; a shari’a tsakanin Jihar Kaduna Da John Moses, inda aka same shi da laifin fyade da zina da ‘yar cikinsa, karkashin sashe na 258 (1) na kundin dokokin Penal Code na shekarar 2017 da aka gyara, sannan aka yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya da yanke mazakuta.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...