Yanzu-yanzu: NNPP ta dakatar da Sanata Kawu Sumaila da wasu yan Majalisar wakilai a Kano

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Jam’iyyar NNPP reshen Kano ta dakatar da wasu manyan mambobin ya hudu da suka hada da Sanata Kawu Sumaila, Ali Madakin Gini, Sani Abdullahi Rogo, da Kabiru Alhassa Rurum, bisa zarginsu da yiwa jam’iyyar zagon kasa.

Kadaura24 ta rawaito Shugaban jam’iyyar na jihar Kano Hashimu Suleiman Dungurawa ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

A cewar Dungurawa, an zabi wadannan ‘yan majalisar dokokin ne a karkashin jam’iyyar NNPP amma a kwanakin baya suna yin wasu abubuwa da suka saba da Manufofi da akidar jam’iyyar.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce an ba su tikitin takara a jam’iyyar gabanin zabukan da suka gabata, amma maimakon su nuna godiya, sai suke yin abubuwan da suka ci karo da muradun jam’iyyar.

Wani lamari na baya-bayan nan da ya janyo dakatarwar shi ne yadda aka gudanar da daurin auren diyar Sanata Kawu Sumaila da kuma bikin yaye ɗaliban jami’ar kawu Sumaila.

Dungurawa ya bayyana mamakinsa da cewa wadanda suka halarci taron galibinsu mutane ne da su ka yaki Kawu a baya, amma kuma ya gayyatosu harkarsa kuma ya ki gayyatar ‘yan jam’iyya NNPP.

Sabon Rikici Ya Kunno Kai Cikin Jam’iyyar APC a Kano

Shugaban jam’iyyar ya bayyana cewa za a kafa kwamitin da zai binciki lamarin tare da sanar da al’umma sakamakon karshe da jam’iyyar za ta dauka.

Duk da dakatarwar, Dungurawa ya jaddada cewa har yanzu akwai sauran damar tattaunawa ga wadanda aka dakatar din, idan har suka nemi afuwa jam’iyyar za ta iya yafe musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...