Rikicin APC: Abdullahi Abbas ya mayarwa da Minista Abdullahi Ata Martani

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Shugaban jam’iyyar APC na jihar Kano Abdullahi Abbas ya mayarwa da ministan ma’aikatar gidaje na Najeriya, Yusuf Abdullahi Ata, martani.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta ruwaito cewa Yusuf Abdullahi Ata ya yi barazanar ficewa daga jam’iyyar APC muddun aka sake zaɓen Abdullahi Abbas a matsayin shugaban jam’iyyar na jihar a karo na hudu.

Amma da yake mayar da martani, sai Abdullahi Abbas ya ce Ata ‘ba dan jam’iyyar ba ne’ sannan sun yi mamakin dalilan da ya sa aka dauko shi har aka ba shi mukamin minista.

InShot 20250115 195118875
Talla

Abdullahi Abbas ya bayyana hakan ne a wata hira da suka yi da BBC Hausa a Kano.

‘Abbas ya ce, ‘Mu a wajenmu ‘yan jam’iyya, dama ban dan jam’iyya bane, a Kano gaba daya a karamar hukumarsa ne mu ka yi na uku ”

”Kuma ba mu sani ba aka bashi minista kuma har shugaban kasa mu gaya wa cewa ba dan jam’iyyarmu bane, anti party ya yi muna.

Manyan Kusoshin NNPP da ‘yan majalisu na shirin dawowa APC – Ganduje

Abdullahi Abbas ya kara da cewa sun yi mamakin mukamin minista da shugaba kasa ya ba shi.

”Muna mamakin yadda aka yi wannan abun wallahi, dan siyasa ne na karamar hukuma kawai”

Abdullahi Abbas ya ce shi burinsa ya zama gwamnan Kano ba sake zama shugaban jam’iyyar APC ba a jihar ta Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...