Gwamnan Kano ya lashe lambar yabo ta gwamna mafi ƙwazo a Afirka

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya kashe lambar yabo ta “Gwarzon Gwamna na Afirka na Shekara” a fannin kyakkyawan shugabanci a bikin bayar da lambobin yabo Karo 14 na mujallar African Leadership Magazine (ALM) da aka gudanar a Casablanca, Morocco.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin, ya fitar a madadin wasu masu taimaka wa shugabannin Afirka da suka halarci taron a Otal din Marriot, Casablanca.

InShot 20250115 195118875
Talla

Wannan girmamawa ta nuna irin nagartar shugabancin Gwamna Yusuf wajen inganta gaskiya, adalci da shugabanci na kowa da kowa, acewar sanarwar.

Acewar Sanusi, Bature, sauye-sauyen da gwamnatinsa ta kawo a fannin ilimi, gine-gine, kiwon lafiya, da bunkasa tattalin arziki sun sanya Jihar Kano zama abin koyi wajen kyakkyawan shugabanci a Afirka.

Rikicin APC: Abdullahi Abbas ya mayarwa da Minista Abdullahi Ata Martani

Gwamnan ya samu wakilcin mai ba shi shawara kan harkokin jiha, Alhaji Usman Bala, wanda tsohon shugaban ma’aikata ne. Gwamnan ya mika wannan lambar yabo ga al’ummar Kano, yana jaddada rawar da suka taka wajen cimma nasarorin da gwamnatin ke samu.

A cewar mujallar African Leadership Magazine, a karkashin jagorancin Gwamna Yusuf, Kano ta samu manyan nasarori ciki har da ware fiye da kashi 31% na kasafin kudin jihar ga fannin ilimi, tallafa wa dalibai masu karatun digiri na biyu a kasashen waje, da kuma amfani da fasahar zamani wajen gudanar da mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...