Inganta ilimi: Jaridar New Telegraph ta Karrama Gwamnan Kano

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya zama Gwarzon Gwamnan da ya fi hidimtawa ilimi a shekarar 2024 na jaridar New Telegraph..

Da yake mika lambar yabo ga Gwamna Yusuf, tsohon Gwamnan Jihar Abia Sen. Orji Uzor Kalu wanda shi ne Mawallafin Jaridar New Telegraph tare da Tsohon Gwamnan Jihar Edo, Kwamared Sen. Adams Oshumole, sun yabawa Gwamna Yusuf bisa kokarin da yake na inganta harkokin ilimi a jihar Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sanusi Bature ya aikowa Kadaura24 ta bayyana cewa, bikin karramawar Manajan Darakta na NNPP Mele Kyari da wasu manyan mutane suka halarta sun bayyana Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin jigo wajen inganta ilimi a kasar nan.

Gwamna Yusuf wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin cikin gida Usman Bala tsohon shugaban ma’aikata a jihar da kwamishinan yada labarai na jihar Kwamared Ibrahim Waiya da wasu manyan jami’an gwamnati sun bayyana matukar farin ciki da karramawar.

Sanarwa ta musamman ga masu neman shiga aikin dansanda

Ya kuma bayyana kudurinsa na ci gaba da baiwa bangaren ilimi kulawa da goyon baya domin cimma burin da gwamnatinsa ta dauka na kawo sauyi a fannin ilimi.

An zabi Gwamna Yusuf ne tare da wasu gwamnonin Najeriya bakwai da suka hada da Ekiti, Sokoto, Lagos, Ondo, Ogun, Borno, Delta da Osun.

An zabi gwamnan jihar Kano ne bisa alkawuran da gwamnatinsa ta dauka na gyara harkokin ilimi da suka hada da ayyana dokar ta-baci kan ilimi, daukar nauyin dalibai 1,001 da suka kammala karatun digiri a kasashen waje, daukar malamai, samar da ajujuwa, kayan koyarwa, da ware kashi 29.5 da kashi 31 cikin 100 na kasafin kudi na 2025 ga bangaren ilimi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...