Na yi nadamar soke nasarar da Abiola ya samu a zaben 1993 – IBB

Date:

Tsohon shugaban ƙasa Ibrahim Badamasi Babangida ya nemi gafarar jama’ar kasar dangane da soke zaben da Chief MKO Abiola ya lashe a shekarar 1993.

Kadaura24 ta rawaito IBB ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi a wajen bikin kaddamar da littafin da ya wallafa na tarihin rayuwarsa, wanda ya samu halartar kusan ɗaukacin tsoffin shugabannin ƙasa da shugaba mai ci Bola Tinubu.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce lokaci ya yi da zai bada na shi ba’asi kan abubuwan da suka faru da kuma matakan da suka dauka, Babangida ya kara da cewa, ”Na yi nadamar soke zaben 12 ga watan Yunin shekarar 1993.

A matsayi na na shugaban ƙasa a lokacin, na ɗauki alhakin duk wani abin da ya faru a karkashin jagoranci na.

Majalisar Malamai ta yanke hukuncin kan danbarwar masallacin Sahaba dake kundila

Tsohon shugaban ƙasa Janar Olusegun Obasanjo ya jagoranci bikin, yayin da shugaba Tinubu ya zama babban bako na musamman.

Sauran bakin da suka halarci bikin sun hada da Tsohon shugaban ƙasa Janar Yakubu Gowon da Abdulsalami Abubakar da Goodluck Jonathan.

Sauran sun hada da tsoffin mataimakan shugaban ƙasa Atiku Abubakar da Namadi Sambo da kuma Yemi Osinbajo wanda ya yi ta’alikin littafin. Sauran sun hada da tsohon shugaban Ghana, Nana Akufo Addo da Ernest Bai Koroma na Saliyo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...

Zaben 2027: Kwankwaso ya bugi kirji

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya...

Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Daga Sharifiya Abubakar   Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro...

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

  Yusuf Galambi dan majalisar wakilai ya sauya sheka daga...