Majalisar Malamai ta yanke hukuncin kan danbarwar masallacin Sahaba dake kundila

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban majalisar malamai ta Kasa Sheik Ibrahim Khalil ya bayyana cewa bayan zama da dukkanin bangarorin da danbarwar Sabon masallacin Sahaba dake kundila a Kano, majalisar ta yanke hukuncin na karshe a kan rikicin.

” Mun yanke hukuncin Sheikh Muhammad Bn Othman zai koma masallacinsa na Sahaba , shi kuma mai kifi da sauran mutanensa za su cigaba da rike na su masallacin na jami’urrahman”.

InShot 20250115 195118875
Talla

Malam Ibrahim Khalil ya bayyana hakan ne lokacin da yake bayyana sakamakon zaman da suka yi ga manema labarai a Kano.

Yadda Gwamnan Kano ke shirin zamanantar da sanaar fawa – Hon. Sani Rabi’u Rio

Ya ce Sheikh Muhammad Bn Othman ya Amince zai cigaba da jagorantar sallah a tsohon masallacinsa na Sahaba dake kundila, yayin da su kuma su mai kifi za su cigaba da gudanar da harkokin masallacinsun na jami’urrahman.

Ya kuma godewa dukkanin jami’an tsaro musamman DSS saboda rawar da suka taka wajen tabbatuwar wannan sulhun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...