A bai-bai aka fahimci kalaman da na yi akan gwamnatin Tinubu – Sarki Sanusi II

Date:

Sarkin Kano na 16 Muhammad Sanusi II, ya bayyana takaicinsa akan yadda aka sauya masa kalamai cewa ba zai taimaki gwamnatin shugaba Tinubu ba domin aiwatar da tsare-tsarenta.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafin X, Muhammadu Sanuni II ya ce dogon jawabin da ya yi ne aka gutsure zuwa rubutun da bai wuce sakin layi ba.

Sarkin Kano na 16 ya ce jawabinsa na goyon bayan tsare-tsaren gwamnatin Tinubu ne kuma ya jinjina wa ‘yan Nijeriya akan hakurin da suka yi na wadaka da dukiyarsu a baya.

InShot 20250115 195118875
Talla

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito Sarki Sanusi ya bayyana cewa ba zai taimakawa gwamnatin Tinubu da shawarwarin da za su taimaka mata ba, saboda abokansa na cikin gwamnatin sun ki su taimaka masa.

Daga bisani ne dai gwamnatin tarayya ta bakin ministan yada labarai Muhammad Idris ta ce Sanusin ya rike shawararsa ba sa bukata.

Ban san ta yaya APC za ta iya karbar mulkin Kano a hannun Abba Gida-gida ba -Abubakar Adamu Rano

A sabuwar sanarwar da Sarki Sanusi II ya fitar ya ce an jima ana Sauya masa magana idan ya yi, inda ya ce wannan ba shi ne karon farko ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...