Manufofi 4 da nake son cimma a matsayin shugaban raya kogunan Hadejia – Jama’are – Rabi’u Sulaiman Bichi

Date:

 

Shugaban hukumar raya kogunan Hadejia – Jama’are Engr. Rabi’u Sulaiman Bichi ya bayyana wasu kudirori da yake son aikawatarwa da zarar ya fara aiki a hukumar domin ciyar da jihohin Kano Jigawa da Bauchi gaba ta fuskar aikin noma.

” Duk da dai ban shiga Ofis ba, amma na gudanar da bincike kuma na tsara wasu kudirori kusan guda 3 zuwa 4 da nake son aiwatar da su, domin ganin Mun dawo da martabar harkokin noma kamar yadda shugaban ƙasa Bola Tinubu yake fata”.

Rabi’u Sulaiman Bichi ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da wakilin jaridar kadaura24 a Kano.

Talla

Sabon Shugaban hukumar ya ce zai zo da tsarin da zai ba da damar inganta takin gargajiya da ake amfani da shi, ta yadda zai zama yana yiwa manoma aiki yadda ya kamata, ba kamar yadda ake amfani da shi a baya ba.

” Batun irin za mu yi kokari mu ga Mun samar da ingantaccen irin wanda zai taimaka manoma su sami amfani mai kyau kuma mai yawa, domin akwai irin shuka kala-kala da ake da shi , musamman a kasashen da suka ci gaba to zamu samar da hanyoyin da manoma za su rika samun iri mai kyau kuma cikin sauki”. Inji MD Hadejia – Jama’are

Bayan NNPCL ya gyara matatar mai ta Warri, Tinubu ya yabawa kamfanin

Ya ce zai tabbatar da cusa son harkokin noma a zukatan Matasan jihohin Kano Jigawa da Bauchi, ta hanyar koya musu harkokin noma da kuma tabbatar da sun sami tallafin da ya dace daga hukumomin da suka chanchanta.

Sabon Shugaban hukumar ta raya kogunan Hadejia – Jama’are akwai damammaki masu yawa da ya kamata manoma su rika amfana da su amma ba sa samu Saboda wasu matsaloli, Amma ya ba da tabbacin yin duk mai yiwuwa don ganin manoman wannan jihohin sun amfana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...