Dr. Yusuf Jibril JY ya taya Ganduje Murnar Cika shekaru 75

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Tsohon kwamishinan harkokin Noma na jihar Kano Dr. Yusuf Jibril JY ya taya Shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje murnar cikarsa shekaru 75 da haihuwa.

” Tabbas Dimokaradiyyar Nigeria zata dade tana amfana da irin gudunmawar da Ganduje ya bayar wajen dorewarta, don haka muke alfahari da shi”.

Dr. JY ya bayyana hakan ne cikin Sakonsa na taya Ganduje murna wanda ya aikowa Kadaura24.

Talla

“A matsayinsa na shugaban jam’iyyarmu ta APC na ƙasa, Ganduje ya hada kan yan jam’iyyar a fadin ƙasar nan, wanda hakan yasa jam’iyyar take samun nasarori a zabukan cike gurbi da aka yi a ƙasar”. Inji Dr. Yusuf Jibril JY

Tsohon kwamishinan harkokin Noman ya ce a madadinsa da iyalansa da magoya bayansa yana taya Dr. Abdullahi Umar Ganduje murnar zagayowar ranar da aka haife shi.

Kwankwaso zai lashe zaɓe da ratar sama da ƙuri’a miliyan 3 PCC

” Muna addu’ar Allah ya kara masa lafiya da kwarin gwiwar cigaba da hidimtawa dimokaradiyyar Nigeria, da kuma ciyar da jam’iyyarmu ta APC gaba”.

Ya ce a karkashin shugabancin Ganduje Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta gudanar da zabuka 5 wadanda ba a yi a yayin babban zaɓen kasa ba, inda ya ce APC ta yi nasara lashe zabuka 4 cikin guda biyar da aka gudanar.

.An haifi Dr. Ganduje ne a ranar 25 ga Disamba, 1949, don haka a wannan rana ta Laraba bikin cika shekaru 75 a duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...