Kotun Ƙoli ta kori ƙarar da ke neman ta sauke Tinubu daga shuagaban Nigeria

Date:

 

 

Kotun Ƙolin Nijeriya, a yau Litinin ta yi watsi da karar da ke neman ta tsige shugaba Bola Tinubu daga mukaminsa.

Kotun kolin, a wani mataki na bai-ɗaya da wasu alkalai biyar su ka yanke, ta kuma ci tarar Naira miliyan 5 akan wanda ya shigar da karar, Cif Ambrose Owuru, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Hope Democratic Party, HDP, a zaben 2019.

Kwamitin wanda mai shari’a Uwani Musa Abba-Aji ta jagoranta, ya kuma gargadi ofishin gudanar wa na kotun koli da kada ya sake karbar duk wata ƙara daga mai karar.

Talla

A shari’ar da ya shigar kai tsaye a kotun koli, Owuru, a cikin wasu zarge-zarge, ya yi zargin cewa shugaba Tinubu ma’aikaci ne na Hukumar Leken Asiri ta Amurka (CIA), matsayar da ya ce ta sa shi ya sanya shi zama shugaban kasa.

Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya aike da suneyen wadanda zai nada Kwamishinoni ga Majalisar jihar

Hakazalika mai shigar da karar ya bukaci kotun kolin da ta haramtawa Tinubu takara bisa zargin ya taba mayar da dala 460,000 ga gwamnatin Amurka a shari’ar da ta shafi miyagun kwayoyi.

Ya kuma roki kotun koli da ta yi amfani da sashe na 157 na kundin tsarin mulkin kasar na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, sannan ta kori Tinubu daga mukaminsa saboda kasancewarsa karkashin ikon hukumomin kasashen waje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...