Majalisar Dattawa ta dakatar da batu kan kudirin dokar Harajin Tinubu

Date:

Daga Sani Idris maiwaya

 

Majalisar Dattawan Nigeria ta ce ta dakatar da yin wani aiki akan dokar Harajin da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya aike mata da shi.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito batun dokar harajin ya jawo ce-ce ku-ce akan kudirin dokar, wanda yan Arewacin Nigeria suke ganin idan aka tabbatar da dokar zata cutar da yankin sosai.

 

Mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Barau Jibrin ne ya sanar da hakan lokacin zaman majalisar na ranar Laraba.

Sanata Barau ya ce an umarci kwamitin kuɗi na majalisar ya dakatar da aikin da yake yi har sai wani kwamiti na musamman ya zauna da babban lauyan ƙasa kan kudirin dokar.

A makon da ya gabata ma majalisar wakilai ta Nigeriya ta dakatar da magana a akan batun dokar har illa-masha-Allah, sakamakon dambarwar da ta faru akan batun dokar harajin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...