Mai Maganin Gargajiya Ya Harbi Kansa Yayin Gwajin Maganin Bindiga

Date:

Wani mai maganin gargajiya, Ismail Usman, ya ɗirka wa kansa harsashi a lokacin da yake gwajin maganin bindiga.

Daily Trust ta ruwaito cewa, lamarin ya faru ne a yankin Kuchibiyi da ke Karamar Hukumar Bwari a Abuja.

Wani mazauni a yankin, Samson Ayuba, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Alhamis yayin da mutumin ya ɗirka wa kansa harsashi a cikin a ƙoƙarin gwada ingancin maganin bindigar da ya haɗa.

Talla

Samson ya ce sai makwabta ne suka yi gaggawar kai mutumin asibiti bayan ya faɗi ƙasa wanwar yana shure-shure.

Rundunar ’yan sandan Abuja ta bakin mai magana da yawunta, Joesephine Adeh ta tabbatar da faruwar lamarin.

Josephine ta ce sun samu kira kan cewa wani mai maganin gargajiya ya harbi kansa a daidai lokacin da yake gwajin ƙarfin maganin bindigar da ya haɗa.

Zargin bata suna: Shugaban NAHCON ya nemi dayyar Naira biliyan daya

Ta bayyana cewa a yayin da yake gwajin sai maganin ya gaza ba shi kariya inda ya ɗirka wa kansa harsashi.

Josephine ta ƙara da cewa tuni aka garzaya da mai maganin gargajiyar asibitin Kubwa domin duba lafiyarsa kafin daga bisani aka aika shi asibitin ƙwararru da ke Gwagwalada domin samun ƙarin kulawa.

Jami’an tsaron sun bayyana cewa bayan sun gudanar da bincike a gidansa, sun gano wata bindigar gargajiya da layu a gidansu waɗanda ya yi amfani da su wurin gwajin maganin bindigar.

‘Yan sandan sun kuma ce a halin yanzu suna ci gaba da gudanar da bincike kuma za su gurfanar da shi a gaban kotu bisa zarginsa da mallakar makami ba bisa ƙa’ida ba da kuma yunƙurin kashe kansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...