Kotun daukaka ta yanke hukunci kan hurumin kotun tarayya na sauraron Shari’ar zaɓen kananan hukumomi

Date:

 

 

Kotun daukaka kara a Abuja ta soke hukuncin kotun tarayya da ke Abuja, wanda ya hana Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) fitar da rajistar masu kada kuri’a ga Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Rivers (RSIEC) domin gudanar da zaben kananan hukumomi na jihar.

A ranar 30 ga Satumba, mai shari’a Peter Lifu na kotun tarayya ya dakatar da INEC daga mika rajistar masu kada kuri’a ga RSIEC.

Yawan ciyo bashi: Atiku ya gargaɗi Tinubu

Haka kuma, alkalin ya hana Hukumar ’Yansandan Najeriya da sauran hukumomin tsaro bayar da tsaro yayin gudanar da zaben.

Talla

Sai dai, yayin yanke hukunci kan daukaka kara da aka shigar kan hukuncin kotun tarayya, mai shari’a Onyekachi Otisi, wanda ya jagoranci kwamitin musamman na kotun daukaka kara, ya bayyana cewa kotun tarayya ba ta da hurumin sauraron karar.

Otisi ya kuma yanke cewa batun karar bai kamata a kai shi gaban kotun tarayya ba. Ya kara da cewa kotun ba za ta iya yanke hukunci kan batutuwan da suka shafi zaben kananan hukumomi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...