Yan sanda sun kama mijin matar da ya zargi Kwamishina da kula matarsa

Date:

Kwana guda bayan Kotun Shari’ar Musulunci ta wanke Kwamishinan Jigawa Auwal Sankara, daga zargin yin lalata da matar aure, ƴansanda a Kano sun kama Nasir Buba, tsohon mijin wacce ake zargin tana soyayya da kwamishinan, Tasleem Baba-Nabegu.

An kama Buba ne a kofar ofishin lauyan sa a jiya Talata.

Jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa hukumar Hisbah ta jihar Kano kwanan nan ta kama Sankara ta tsare shi bayan Buba ya kai karar cewa kwamishinan na neman matarsa.

Talla

Buba ya shigar da kara a kotun Shari’a bisa zargin.

Sai dai a zaman kotun na ranar Litinin, alkalin kotun, Ibrahim Sarki-Yola, ya yi hukuncin wanke Kwamishinan bisa rahoton binciken da ofishin Mataimakin Sufeto Janar na ƴansanda, shiyya ta 1 a Kano ya gabatar.

Ƴansanda sun bayyana cewa bisa bincikensu, ba su samu wani shaidar da za ta tabbatar da zargin zina a kan wanda ake zargi ba.

Nan gaba Kadan za a rasa dan Kwankwasiyya a kananan hukumomin Ghari da Tsanyawa – Sani Bala Tsanyawa

Bayan kotun ta wanke zargin, sai kuma reshe ya JUYE da mujiya, inda ƴansanda su ka kama mijin matar, Buba, a jiya Talata bisa zargin yi wa matarsa kutse a wayar salular ta.

Majiyoyi sun bayyana cewa Buba ya samo bayanai da dama daga wayar matarsa don yin amfani da su wajen tabbatar da zargin da ya gabatar a kan kwamishinan.

“Gaskiya abin ya nuna cewa ‘yansanda suna da bangaranci a wannan lamari. Nasir ya gabatar da hotuna, bidiyo, saƙonnin rubutu da muryoyi da ke nuna hujjar alakar soyayya tsakanin kwamishinan da matar,” in ji wata majiya da ke da masaniya game da al’amarin.

“Abin mamaki ne yadda ‘yansanda suka wanke kwamishinan sannan suka kama wanda ya kai karar bisa zargin bata suna ta yanar gizo.”

Da aka tuntube shi, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Kiyawa, ya ce ba a sanar da shi wannan ci gabanba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...