Yadda kananan yara su ka jagoranci zaman majalisar dokokin jihar kano

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Yayin da majalisar dinkin duniya ta ware ranar 20 ga watan Nuwanba na kowacce shekara a matsayin ranar yara ta duniya, a yau laraba wasu kananan yara sun jagoranci zaman majalisar dokokin jihar kano.

A yayin Zaman majalisar na wannan rana an gabatar da kudirori da dama wadanda suka shafi al’umman kananan yara, Ilimi, da dai sauransu.

Wani yaro mai suna Muhammad Isa shi ne ya jagoranci zaman majalisar a matsayin shugaban majalisar.

Talla

Da yake zantawa da wakilin kadaura24, Muhammad Isa ya ce Yau wata rana ce da ba zai taba mantawa da ita ba, domin ya zauna a kujerar da take da muhimmancin gaske a tsarin mulkin al’umma.

Sarkin Musulmi ya bayyana dalilin da ya sa ake ganin kamar sarakuna na tsoron gwamnoni

” Ina gode wa majalisar dinkin duniya da ta ware mana wannan yara a matsayinmu na yara, masu tasowa, tabbas wannan rana dole mu yi alfahari da ita sosai”. Inji Shugaban majalisar

Suma wasu daga cikin yaran da suka gudanar da zaman majalisar sun bayyana jin dadinsu bisa damar da suka samu na zaman a zauren majalisar dokokin jihar kano albarkacin Ranar yara ta duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...