Dalilin da ya sa Tinubu ya dage taron majalisar zartarwar kasa – Fadar Shugaban Kasa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake dage zaman majalisar zartarwa ta tarayya bayan rasuwar babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja.

Shugaban ya bayyana cewa daga baya za a bayyana sabuwar ranar da za a gudanar da taron.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar.

Talla

Ya rubuta: “Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin dage taron majalisar zartarwa ta tarayya har zuwa wani lokaci da za a bayyana nan gaba.

Kotu ta hana CBN riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano

Sanarwar ta ce Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin sassauta tutar Nigeriya zuwa Rabi har na tsahon Kwanaki 7 a duk fadin kasa saboda girmamawa ga Babban hafsan sojin.

Idan za a iya tunawa da safiyar wannan rana ce ta Laraba fadar shugaban kasar Nigeriya ta bayar da sanarwar mutuwar Taoreed Lagbaja babban hafsan sojin kasa na Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...