Gwamnan Kano Ka Cire Kwamishiniyar Jin Kai Saboda Za ta Jawo Maka Bakin Jini – Anas Abba Dala

Date:

Daga Buhari Ali Abdullahi

 

Babban Mai taimakawa gwamnan jihar kano na musamman kan wayar da kan al’umma ta fuskar Siyasa Hon. Anas Abba Dala ya roki gwamnan Abba Kabir Yusuf da kori kwamishiniyar ma’aikatar jin kai Hajiya Amina HOD saboda zargin da Ake yi Mata na cin zarafin wata likita.

“Abun da ake zargin kwamishiniyar da shi ba dabi’ar gwamnanmu ba ce , kuma hakan zai zubar da kimar gwamnati da ta gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Kasance

Anas Abba Dala ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da jaridar kadaura24 ranar litinin.

Talla

Ya ce akwai bukatar gwamnan jihar kano ta Fara dakatar da ita sannan kasa a binciki lamari, idan har an same ta da laifi sai a hukuntata bayan a koreta daga mukamin kwamishiniya.

“Gwamnan Kano mutum ne mai mutunci da kyamar cin zarafin al’umma saboda hakan ba dabi’arsa ba ce, don haka bai kamata a sami wani daga cikin Jami’an gwamnatinsa da wannan mummunar dabi’ar ba”. Inji Anas Abba Dala

Yadda rikicin NNPP Kano ya kara ruruwa yayin da Gwamna Abba ya daina daga wayar Kwankwaso

Ya ce yana da yakinin gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf zai ba da umarnin bincika wannan al’amari don gano mai gaskiya tare da daukar matakan da suka dace akan mara gaskiya.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito kungiyar likitoci ta jihar kano ta yi kira ga gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da ya kori kwamishiniyar ma’aikatar jin kan al’umma bisa zarginta da cin zarafin wata likita a asibitin kwararru na Murtala Muhammad dake Kano.

Sai dai a wani martani da ta yi kwamishiniyar Hajiya Amina Abdullahi HOD ta ce Kiran da likitoci suka yiwa gwamnan Kano na ya cire ta bai firgita ta ba, saboda abun da ya yi ta yi shi ne akan aikinta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...