Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin Sarautar Sarkin Gwandu

Date:

Ƙotun ɗaukaka ƙara a Najeriya ta ce Alhaji Mustapha Haruna Jokolo ne sarkin Gwandu da ke Jihar Kebbi, saboda a cewarta ba a bi ƙa’ida ba wajen sauke shi daga sarautar da aka yi.

Alkalin kotun da ke zama a Sokoto Ibiowei Tobi, ya sake tabbatar da hukuncin da babbar kotun jihar Kebbi ta yi cewar gwamnatin jihar ta wancan lokaci ta saba ka’ida wajen matakan da ta ɗauka na sauke Sarkin Gwandu na 14 daga karagar mulki.

Saboda haka kotu ta yi watsi da ƙarar da gwamnatin jihar Kebbi ta gabatar a gaban ta, domin neman halarta matakan da ta bi wajen sauke sarkin.

Talla

Da wannan hukunci yanzu kallo ya koma kotun ƙoli wadda ake saran ta yanke hukunci na ƙarshe dangane da wannan shari’a, da aka kwashe sama da shekaru 20 ana tafkawa.

Ƙotun ɗaukaka ƙara a Najeriya ta ce Alhaji Mustapha Haruna Jokolo ne sarkin Gwandu da ke Jihar Kebbi, saboda a cewarta ba a bi ƙa’ida ba wajen sauke shi daga sarautar da aka yi.

RFI

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar cigaban Ilimi da gyaran tarbiya ta unguwar zango ta shirya taron kan tarbiyya da tsaro

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malami a jami'ar Bayero dake...

Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da...

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...