Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin Sarautar Sarkin Gwandu

Date:

Ƙotun ɗaukaka ƙara a Najeriya ta ce Alhaji Mustapha Haruna Jokolo ne sarkin Gwandu da ke Jihar Kebbi, saboda a cewarta ba a bi ƙa’ida ba wajen sauke shi daga sarautar da aka yi.

Alkalin kotun da ke zama a Sokoto Ibiowei Tobi, ya sake tabbatar da hukuncin da babbar kotun jihar Kebbi ta yi cewar gwamnatin jihar ta wancan lokaci ta saba ka’ida wajen matakan da ta ɗauka na sauke Sarkin Gwandu na 14 daga karagar mulki.

Saboda haka kotu ta yi watsi da ƙarar da gwamnatin jihar Kebbi ta gabatar a gaban ta, domin neman halarta matakan da ta bi wajen sauke sarkin.

Talla

Da wannan hukunci yanzu kallo ya koma kotun ƙoli wadda ake saran ta yanke hukunci na ƙarshe dangane da wannan shari’a, da aka kwashe sama da shekaru 20 ana tafkawa.

Ƙotun ɗaukaka ƙara a Najeriya ta ce Alhaji Mustapha Haruna Jokolo ne sarkin Gwandu da ke Jihar Kebbi, saboda a cewarta ba a bi ƙa’ida ba wajen sauke shi daga sarautar da aka yi.

RFI

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...