Gaskiyar Lamari Game da Lokacin Dawo da Wutar Lantarki a Arewacin Nigeria

Date:

 

Kamfanin Samar da Wutar Lantarki a Nijeriya (TCN) ya ce babu takamaiman lokacin dawo da wutar lantarki da aka ɗauke a sassan yankin Arewa ba.

TCN ya ce duk da cewa ana ƙoƙarin gyara wutar, amma matsalar rashin tsaro ta sa ba za a iya ci gaba da aikin gyaran ba.

Babbar jami’ar TCN, Nafisatu Asabe Ali, ta ce kamfanin ya samu takardar gargaɗi daga Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro cewa akwai haɗarin gaske shiga yankin da aka lalata manyan turakun lantarki uku, saboda matsalar rashin tsaro.

Yan Sanda a Kano sun bayyana matsayarsu kan hukuncin Kotu game da zaben kananan hukumomin

Ta ce ci gaba da cewa duk da cewa kamfanin ya riga ya tanadi kayan aikin gyaran, amma ba zai iya shiga wajen ba, sai ya ki daga hukumomin tsaro.

Kimanin kwanan huɗu a jere ke nan da aka ɗauke wutar bayan lalacewar babban layin lantarkin Shiroro zuwa Manzo, wanda ke isar da wutar ga akasarin yankin Arewa.

Yadda Togo da Benin suke samun wutar lantarki sa’a 24 daga Nigeriya

Bayan lalacewar layin ne TCN ya yi ƙoƙarin amfani da layin Ugwaji zuwa Apir zuwa .mai karfin 330kV domin tura wuta zuwa yankin, amma aka yi rashin sa’a shi ma ya lalace.

 

TCN ya bayyana cewa matsalar ta jefa jihohin Arewa maso Gabas da arewa maso Yamma da wani yanki na Arewa ta Tsakiya cikin duhu.

Talla

Injiniya Nafisa ta bayyana cewa har yanzu babban layin Shiroro ba ya aiki, kuma ba za a iya cewa ga takamaiman lokacin da za a gyara shi ba saboda matsalar tsaro.

Ta ci gaba da cewa ko da an gyara layin Ugwaji zuwa Apir mai karfin 750, ƙarfin wutar da zai iya dauka a yanzu bai wuce 350kV.

Don haka sai dai a ba wa wasu yankunan jihohin Kano da Kaduna da Jamhuriyar Nijar.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...

Zargin kwace gona: Majalisar Dokokin Kano zata binciki Shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada (ALGON)

    Majalisar dokokin jihar Kano, ta sha alwashin gudanar da...