Yadda Togo da Benin suke samun wutar lantarki sa’a 24 daga Nigeriya

Date:

Manajan darakta kuma babban jami’in gudanarwa na Hukumar Rarraba wutar lantarkin Najeriya TCN, Sule Abdulaziz ya ce ƙasashen Togo da Benin suna samun wutar lantarki ta sa’a 24 daga Najeriya.

“Muna ba Togo da Benin da Nijar lantarki. Suna samun wutar awa 24, kuma suna biya,” in ji Abdulaziz a tattaunawarsa da tashar talabijin ta Channels a ranar Lahadi.

Talla

Da aka tambaye shi dalilin da ya sa ƴan Najeriya da dama ba sa samun wutar kamar haka, sai ya ce, “Yan Najeriya na samun wuta sosai amma ba a ko’ina ba. Waɗanda suke Band A suna samun lantarki na tsakanin awa 20 zuwa 22 a rana,” in ji shi.

Gwamna Abba ya taya Kwankwaso cika shekaru 68 a duniya

Abdulaziz ya ƙara da cewa, “ina tabbatar muku za mu iya fara samun isasshiyar wutar lantarki nan da shekara biyar. Sabon ministan yana ƙoƙari domin tabbatar da hakan.”

Ya ƙara da cewa akwai bambanci tsakanin TCN da Nepa, “lokacin da muke Nepa, mu ne muke samar da wutar, mu rarraba, sannan mu yi kasuwancinta, amma yanzu rarraba wutar kawai muke yi,” in ji shi. Sannan ya ƙara da cewa idan aka samu tangarɗa daga babban layin ƙasar, ana ɗora musu laifi ne saboda ana musu kallon Nepa.

Talla

“Idan an samu tangarɗa ba dole ta zama daga TCN ba, domin za a iya samu a sauran ɓangarorin.”

Shugaban na TCN ya kuma bayyana lalacewar kayan aiki, a matsayin wata matsala da ke addabarsu, inda ya ce, “yawancin kayayyakin aikin da muke amfani da su sun haura shekara 50.”

Talla

A game da tsadar lantarki kuwa, Abdulaziz ya ce, wutar lantarki na da sauƙi a Najeriya, idan aka kwatanta da wasu ƙasashen Afirka irin su Burkina Faso da Senegal da Jamhuriyar Nijar.

BBC Hausa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...