Bincike ya gano adadin yawan yan Nigeria da suka talauce a bana

Date:

Bankin duniya ya saki rahoto a kan ci gaban Najeriya, inda yace fiye da ‘yan Najeriya milyan 129 ne ke cikin kangin talauci.

A jiya Alhamis ne bankin duniyan ya saki rahoton a daidai lokacin da hauhawar farashin gaba-dayan kayan bukatu ke kara tashi, abinda ke kara jefa miliyoyin ‘yan Najeriya cikin yunwa.

Talla

A cewar bankin, wannan adadi na fiye da ‘yan Najeriya miliyan 129 na wakiltar tashin gwauron zabo daga kaso 40.1 cikin 100 da aka gani a 2018 zuwa kaso 56 cikin 100 a bana.

An ruwaito rahoton na bankin duniyar na cewa, “sakamakon gazawar bunkasa wajen iya tserewa hauhawar farashi, talauci ya yi tashin gwauron zabo.

Tun a shekarar 2018, an kiyasta cewa adadin ‘yan Najeriya dake rayuwa cikin kangin talauci ya yi matukar karuwa da kaso 40.1 zuwa kaso 56 cikin 100.

Talla

“Idan aka hada da karuwar yawan jama’a, hakan na nufin cewar wasu ‘yan Najeriya miliyan 129 na rayuwa cikin talauci. Wannan karin na nuni da yadda bunkasar Najeriya ke cikin mawuyacin hali. Yanayin bunkasar tattalin arzikin Najeriya bai farfado zuwa mizanin da yake ba gabanin koma bayan arzikin da farashin mai ya sabbaba a 2016.

Talla

Aannobar korona ta sake ta’azzara koma bayan tattalin arzikin kasar.

A cewar rahoton, an samu kari da mutum miliyan 115 a 2023 zuwa 129 a 2024, abinda ke nufin cewa ‘yan Najeriya miliyan 14 sun kara talaucewa a bana.

VOA

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...