Rikicin NNPP: Kar ka saka ni a abun da bai kamata na shiga ba – Kwankwaso

Date:

Daga Sani Danbala Gwarzo

 

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ya yanke shawarar kin cewa komai game da rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar a jihar Kano.

Kwankwaso, da manema labarai suka tambaye shi a gidansa na Miller road da ke Kano da yammacin ranar Talata, ya ce ba shi da wani abin cewa a kan lamarin.

Talla

“Don Allah Bana son yin magana akan wannan batun . Kar ka sa ni cikin abin da bai kamata a na shiga ba. Shugaban jam’iyyar ya yi magana kuma yana magana, ku je gare shi,” Kwankwaso ya fadawa manema labarai.

Sabon Rikici: Jam’iyyar NNPP a Kano ta dare gida biyu

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin jihar Kano, Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da kwamishinan sufuri, Muhammad Diggol daga jam’iyyar.

A cewar Dungurawa, dakatarwar ta biyo bayan korafe-korafensu da ake kaiwa shugabannin mazabunisu da na kananan hukumomi na jam’iyyar.

Talla

Dungurawa ya ce an dakatar da su ne saboda rashin mutunta jam’iyyar da shugabancinta.

Idan za a iya tunawa a yan Kwanakin nan ana ta zargin Sakataren gwamnatin Kano Dr. Baffa Bichi bisa daukar nauyin wata kungiya mai suna ” Abba tsaya da kararka” wacce take rajin ganin an sami farraku tsakanin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa Rabi’u Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...

Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Daga Halima Umar Dogo   Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba...

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...