An baiwa Ganduje wa’adin Kwanaki 7 ya sauka daga mukamin shugaban APC na ƙasa

Date:

 

 

Kungiyar gamayyar kungiyoyin jami’iyyar APC na yankin Arewa ta tsakiyar Nijeriya sun baiwa shugaban jami’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje wa’adin kwanaki 7 da ya yi murabus daga mukaminsa cikin ruwan sanyi.

Talla

Shugaban kungiyar Hon Saleh Abdullahi Zazzaga a taron manema labarai a Jos babban birnin jihar Plateau, ya ce idan wa’adin ya kare Ganduje bai sauka ba, akwai yiwuwar ya dauki matakin shari’a a kansa.

Wannan wa’adi dai zai kare ne a ranar Litinin 14 ga watan Oktoba, 2024.

Cigaban ilimi: An bude makarantu uku da Rarara ya gina

Saleh Zazzaga dai na kalubalantar cewa a babban taron jami’iyyar da ya gudana a ranar 26 ga watan Maris, 2022, an ba yankin Arewa ta tsakiya damar samar da shugaban jami’iyyar APC na kasa.

Talla

Bayan murabus din Abdullahi Adamu wanda ya fito jihar Nasarawa, maimakon a mayar da kujerar a yankin, sai aka ba Ganduje wanda ya fito daga yankin Arewa maso Yammacin Nijeriya, wanda a cewarsa hakan ya saba wa kundin tsarin jami’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...