Sojojin Nijeriya sun sake hallaka kasurgumin dan fashin daji a Katsina

Date:

Dakarun Nijeriya sun sake samun nasarar hallaka kasurgumin dan fashin daji a Katsina.

A wata babbar nasara a yakin da ake yi da ta’ddanci, an kashe kasurgumin dan fashin dajin nan, Sani Wala Burki wanda ke addabar kananan hukumomin Safana da Batsari a jihar Katsina.

Kafar yada labarai mai kawo rahoton tsaro a Arewa, Zagazola Makama ce ta rawaito cewa jami’an tsaro da ‘yan banga na sa kai a jihar Katsina ne suka hallaka dan fashin dajin tare da mayakansa.

Sojojin Nigeria sun Kashe Ƙasurgumin Dan ta’adda da ya addabi Arewacin Nigeria

Lamarin ya faru ne a daren jiya a yayin ‘yan bindigar suka yi yunkurin kai hari ga mazauna garin Safana.

A martanin da suka mayar ‘yan bindigar da suka samu hadin kai da jami’an tsaro sun fuskanci ‘yan bindigar.

 

Acewar mazauna garin, an kashe Burki da mayakansa da dama a yayin fafatawar.

Dole yan Nigeria su dawo daga rakiyar siyasar ubangida wajen zaɓen shugabanni — Shekarau

Sani Wala Burki dai ya shahara wajen kai hare-hare a yankin.

Hakan na zuwa ne bayan sojojin Nijeriya sun kashe kasurgumin dan fashin daji, Kachalla Sububu a jihar Zamfara.

Majiya: Zagazola Makama mai sharhi kan lamuran tsaro a yankin yammancin Afrika.

Daily Nigerian

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...