Zaɓen kananan hukumomin Kano: APC ta fadi matsayarta

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Jam’iyyar APC a jihar Kano tace za ta shiga zaɓen ƙananan hukumomi da za a gudanar a ranar 26 ga watan Oktoba mai zuwa.

A sanarwar da kakakin jam’iyyar, Hon. Ahmad S Aruwa ya fitar yace bayan karbar rahoton kwamitin da ya tattara shawararwari don shiga zaben, jam’iyyar ta yanke hukunci shiga a matsayinta Na jam’iyya mai mulki a Najeriya.

Gwamnatin Kano ta dakatar da tsawaita wa’adin ma’aikata 4,000 da Ganduje ya yi

Sanarwar ta kuma umarci dukkanin masu sha’awar takarar su kai takardar nuna sha’awa ga ofishin jam’iyyar dake kananan hukumomi tun daga ranar 12 zuwa 14 ga watan Satumba.

Idan za’a iya tunawa a kwanakin baya jam’iyyar APC ta jihar kano ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin Rabi’u Sulaiman Bichi, domin su duba yiwuwa jam’iyyar ta shiga zaben ko kar ta shiga.

 

Daga karshe dai a jiya laraba kwamiti ya mika rahotonsa, kuma ga shi a yau jam’iyyar ta amince zata shiga a fafata da ita a zaɓen shugabannin kananan hukumomin dake tafe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...