Da dumi-dumi: Tinubu ya gana da Sarki Charles na Burtaniya

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Sarki Charles III na burtaniya ya tarbi bakuncin Shugaban ƙasar Nigeriya Bola Tinubu a ranar Laraba a fadar Buckingham da ke birnin Landan na Inda suka yi ganawar sirri.

Bayo Onanuga, mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya ce taron ya nuna kyakkyawar alakar da ke tsakanin Najeriya da Burtaniya.

Ya ce wannan shi ne ganawar farko da shugabannin biyu suka yi tun bayan da suka hadu a Dubai a taron COP 28 na yanayi a bara.

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Kano ta Sanya Ranar Komawa Makarantun Firamare da Sakandire

Sanarwar ta ce Sarkin ne ya bukaci ganawa da shugaban Tinubu.

“Shugabannin biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi al’amuran duniya da na shiyyar Africa, inda suka mai da hankali kan kalubalen sauyin yanayi,” in ji Onanuga.

Ya ce Tinubu da Sarki Charles sun kuma binciko damar yin hadin gwiwa tare da sa ran taron COP 29 da za a yi a Azerbaijan da kuma taron shugabannin kasashen Commonwealth (CHOGM) a Samoa.

Amb. Jamilu Bala Gama ya Zama Sabon shugaban kasuwar waya ta Farm Center

Shugaba Tinubu ya sake nanata kudurin Najeriya na ganin an magance matsalar sauyin yanayi ta hanyar da ta dace da manufofin tsaron makamashin kasar yayin da yake tabbatar da shirin Najeriya na daukar dabarun da sauran kasashen duniya ke amfani da shi

Onanuga ya ce “A yayin tattaunawar tasu, shugabannin biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan sabbin hanyoyin samar da kudade tare da bayyana sha’awar juna na karfafa hadin gwiwa ta hanyar amfani da matsayin shugabancin Najeriya a Afirka da kuma Commonwealth,” in ji Onanuga.

Solacebase

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...