Yadda za ku sayi Shinkafar Tinubu akan Naira dubu 40 kowanne buhu

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin tarayya ta bayyana wadanda ya kamata su amfana da shinkafar da zata sayar da kuma hanyoyin da za a abi domin mallakar Shinkafar akan farashin Naira dubu 40 kowanne buhu.

Kadaura24 ta rawaito Dr. Haruna Sule shi ne daraktan tsare-tsare na ma’aikatar aikin gona ta kasa , ya yi bayani dalla-dalla kan yadda al’umma za su amfani shirin.

YANZU-YANZU: Tinubu ya magantu kan karin farashin man fetur Nigeria

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa gwamnatin tarayya ta fara sayar da Shinkafar akan farashin naira dubu 40 kowanne babban buhu domin saukakawa al’umma.

Dr. Haruna Sule ya ce masu karamin karfi da ma’aikatan gwamnatin ne zasu amfana da tsarin sayar da Shinkafar na gwamnatin tarayya.

Ya ce dole ne duk wanda ya ke so ya sayi Shinkafar ta gwamnatin tarayya ya zamana yana da lambar katin shaidar dan kasa wato NIN.

 

Ya ce su kuma ma’aikatan gwamnati za iya siyan Shinkafar ne da lambarsu ta tsarin biyan albashi wato IPPIS.

” Za a biya kuɗin Shinkafar ne ta na’urar ATM Ko Turawa ta banki, sannan duk wanda ya biya za a bashi wata lamba wadda shi kadai yake da ita, ita ce a matsayin shaidar ya biya kuma ita zai nuna ya karɓi Shinkafar da ya siya”.

Man Fetur shi zai rika yiwa kansa farashi yanzu a Nigeriya – NNPC

Dr. Haruna Sule ya kuma ce za a samar da Wuraren sayar da Shinkafar a duk fadin jihohin Nigeria har da Babban birnin tarayya Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...