Kotu ta tusa keyar alƙalin bogi zuwa gidan yari a Kano

Date:

Wata kotun Musulunci ta tisa ƙeyar wani alƙalin bogi zuwa gidan yari a Jihar Kano.

Dubun alƙalin bogin ta cika ne bayan da ya gabatar da kansa a matsayin alkali daga Jihar Jigawa a gaban Kotun Musulunci da ke unguwar Kurma, Ƙaramar Hukumar Fagge.

Yan arewa ku yi mana aikin gafara, mun gaza kare ku – ACF

Asirin alƙalin bogin ya tonu ne a lokacin da ya je kotun neman belin wasu mutane biyu wadanda ake zargi da laifin damfara da cin amana.

Kotun ta amince da ba shi belin mutanen ne a bisa sharaɗin sai ya kai jami’an kotu gidansa, amma nan take ya ƙi amincewa.

 

Da aka tsananta bincike daga baya sai aka gano cewa ungulu da kan zabi ya yi, ma’aikacin shari’a ne, amma bai taɓa zama alkali ba.

Kungiyar Samarin Tijjaniyya sun Allah wadai da kara kudin man fetur a Nigeria

A lokacin da aka gurfanar da shi, ya amsa laifinsa, sannan ya roki alkali ya yi masa sassauci.

Khadi Umar Lawan Abubakar ya ba da umarnin tsare shi a gidan yari zuwa ranar 23 ga watan Satumba, 2024 domin ci gaba da shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...