Badakalar magungunan Kano: Mun fara bincike kuma za mu gurfanar da duk mai hannu – Muhuyi Magaji

Date:

Hukumar karbar korafe-korafe da hana cin hanci da rashawa ta jihar Kano, ta fara bincike kan badakalar sayen magunguna na biliyoyin nairori a kananan hukumomi 44 na jihar.

Shugaban hukumar Muhuyi Rimin-Gado ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ta wayar tarho a Kano ranar Talata.

“Mun fara bincike mai zurfi kan zarge-zargen da ake yi game da samar da magunguna na biliyoyin Naira ga kananan hukumomi 44.

Fadan daba/Tsadar rayuwa: A’lummar Ja’en Makera a Kano sun gabatar da alkunut don neman daukin Allah

Rimin-Gado ya ce “Ko da wanene ke da hannu, za mu gano shi kuma mu hukunta wadanda aka samu da laifi.”

A cewarsa, hukumar na binciken zargin karkatar da kayan abinci da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati Abba Yusuf, Shehu Sagagi ya yi.

Shugaban ya yi kira ga jama’a da su bayar da sahihin bayanai da za su taimaka wajen gudanar da binciken.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Dr. Bello Galadanci wanda aka fi sani da Dan Bello ya bankado wata almundahana kudaden kananan hukumomin Kano 44 da ake fitar wa da sunan siyan magunguna, wanda ake zargin wani makusanci jagoran jam’iyyar NNPP Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da mallakar kamfanin da ake amfani da shi.

Gwamnan Abba Gida-gida ya yi alkawarin samar da Karin birane biyu a Kano

Kadaura24 ta kuma rawaito cewa gwamna Yusuf a cikin wata sanarwa, ya musanta masaniya akan kwangilar da aka ce na samar da magunguna.

Kwamishinan yada labarai, Baba Halilu Dantiye, da Darakta Janar na yada labaran gwamna Sanusi Dawakin-Tofa ne suka sanya hannu akan sanarwar.

Don haka gwamnan ya umurci hukumar da ta gaggauta fara bincike kan lamarin tare da kai rahoton sakamakon domin daukar matakin da ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...