Da dumi-dumi: Tinubu zai tafi ƙasar Equatorial Guinea

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Shugaban kasa Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Malabo na kasar Equatorial Guinea a ranar laraba 14 ga watan Agusta a wata ziyarar aiki ta kwanaki uku

Tinubu zai je kasar ne domin girmama gayyatar da shugaba Teodoro Obiang Nguema Mbasogo ya yi masa.

Dalilin da ya haifar da rikici tsakanin yan bindiga har suka kashe 30 daga cikinsu

Tinubu, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale, ya fitar, zai gana da shugaban kasar Equatorial Guinea a fadar shugaban kasar idan ya da isa, inda za a yi taruka tsakanin shugabannin biyu da kuma kulla yarjejeniyoyin da suka shafi man fetur da iskar gas da kuma tsaro.

Zargin karkatar da shinkafa: EFCC ta karɓi korafi kan shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Kano

Shugaban Najeriyar dai zai samu rakiyar ministan harkokin wajen kasar Ambasada Yusuf Tuggar da sauran mukarraban gwamnatinsa, wadanda za su sa hannu wajen rattaba hannu kan yarjejeniyoyin da kuma nazarin damarmakin inganta alakar da ke tsakanin kasashen biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...