Sakacin jami’an tsaro ne ya sa masu zanga-zanga su ka yi barna a Kano – Sarki Sanusi II

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Mai martaba Sarkin Kano na 16, Alhaji Muhammadu Sanusi II, a ranar Laraba ya koka da barna tare da wawashe dukiyoyin al’umma da aka yi yayin zanga-zangar da tsadar rayuwa a jihar.

” Kafin faruwar wannan lamarin an sanar da jami’an tsaro cewa akwai yiwuwar bata gari zasu farwa wasu daga cikin Kaddarorin gwamnati da na yan kasuwa amma suka ki daukar matakan da suka dace”

Daily trust ta rawaito sarki Sanusi ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ya ziyarci madaba’ar jihar Kano da NCC Digital Industrial Park da kuma Shagunan Barakat wadanda ke cikin kadarorin da na masu zanga-zangar suka lalata .

Talla
Talla

Ya zargi jami’an tsaro da yin sakaci da labarin faruwar lamarin da aka ba su tun kafin faruwar lamarin .

” Kowa yayi da kyau kansa kuma ko ya yi akasin hakan Kansa, muna addu’ar Allah ya baiwa gwamnati ikon gyara Wuraren da aka lalata”.

Ya ce kakansa ya yi aiki da kamfanin buga takardun na Kano inda ya kara da cewa “abin bakin ciki ne yadda jikokinsu suka lalata irin wannan wuri”.

Matasa sun kwashe shinkafa a tsohon gidan wani jami’in gwamnatin Kano

A cewarsa, “Kamar yadda muka saba cewa duk wanda ke da hannu a cikin wannan mugun aikin makiyi ne ga al’ummar Kano .

“Kakana ya yi aiki a nan (kamfanin buga littattafai na Kano). Abin bakin ciki ne yadda jikokinsu suka lalata irin wannan wuri.

“Kafin hakan ya faru, an sanar da jami’an tsaro a rubuce cewa hakan zai faru amma maimakon a hana hakan, sai aka bari hakan ya faru”, in ji shi.

An kafa kamfanin buga littattafai na Kano a shekarar 1938, kuma tun a wancan lokaci take aiki .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...