Jafar Sani Bello ya koka kan kokarin sayar da harabar hukumar ITF ta Kano

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Tsohon dan takarar gwamnan jihar kano a jam’iyyar PDP Alhaji Jafar Sani Bello ya rubuta takardar koke game da yunkurin sayar da harabar hukumar koyawa matasa sana’o’i ta kasa ITF dake jihar kano.

A wasikar da jaridar kadaura24 ta gani mai dauke da kwanan watan 29, ga watan Yuli 2024, Jafar Sani Bello yace ya sami bayanai da suke nuna cewa ana shirin sayar da harabar hukumar wacce aka samar don cigaban jihar kano da al’ummarta.

Talla
Talla

” Na damu sosai dana sa mu sami labarin jami’an hukumar ku ta ITF sun hada kai da wasu masu harkar filaye suna kokarin sayar da harabar hukumar, wanda hakan ba daidai ba ne”.

Da dumi-dumi: Tinubu ya rage farashin Shinkafa a Nigeria

Ya ce sayar da harabar hukumar ta ITF zai kawo cikas ga aiyukan hukumar na ba da horo ga matasa don su dogara da kawunansu .

Jafar Sani Bello ya ce yana fatan hukumar ta ITF ta kasa da ta dakatar da kudirinta na sayar da harabar hukumar da gwamnatin jihar kano ta bata don koyawa matasan jihar sana’o’i .

Talla

Ya ce sayar da harabar hukumar zai cutar da jihar Kano da matasan jihar, domin aikin da aka samar da hukumar don shi zai kadata ko ya sami tasgaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...